Back to the Leicester City Newsfeed

Algeria ta ki gayyatar Feghouli kofin nahiyar Afirka ba

Tawagar kwallon kafa ta Algeria ba ta bai wa Sofiane Feghouli, goron gayyata zuwa gasar cin kofin nahiyar Afirka da kasar za ta buga a Gabon a 2017 ba.

Tun farko an yi hasashen cewar kociyan Algeria, George Leekens, zai gayyaci Feghouli mai taka-leda a West Ham United zuwa gasar da za a fara a ranar 14 ga watan Janairu.

Sai dai kuma kociyan ya gayyato 'yan wasan kasar da suke buga tamaula a gasar Premier da suka hada da Riyad Mahrez da Islam Slimandi masu wasa a Leicester City da kuma Adlene Guedioura na Watford.

Algeria wadda take rukuni na biyu a gasar cin kofin nahiyar Afirka, za ka kara da Tunisia da Senela da kuma Zimbabwe.